Babbar kotun tarayya da ke Abuja ta umarci hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa (INEC) da ta yi wa jam’iyyar Citizens Democratic Alliance (CDA) rijista a matsayin cikakkiyar jam’iyyar siyasa a Najeriya.
Mai shari’a Obiora Egwuatu ne ya bayar da umarnin a ranar Talata yayin sauraron ƙarar mai lamba FHC/ABJ/CS/2787/25 da wasu jagororin ƙungiyar suka shigar kan INEC.
A baya, a watan Oktoban 2025, INEC ta bayyana cewa CDA na cikin ƙungiyoyi takwas da suka cika sharuddan farko na neman zama jam’iyyun siyasa bayan sun gabatar da takardun da ake buƙata.
Sai dai a watan Disamban 2025, an ƙi amincewa da neman rijistar CDA. Daga baya shugaban INEC, Joash Amupitan, ya bayyana cewa ƙungiya ɗaya ce kacal, wato Democratic Leadership Alliance (DLA), ta cika dukkan sharuddan doka kuma aka yi mata rijista.
Masu ƙarar sun garzaya kotu suna zargin cewa CDA ta cika dukkan ka’idojin kundin tsarin mulki da dokokin zaɓe, don haka matakin INEC na ƙin yi mata rijista bai dace ba.
Bayan sauraron ƙarar, kotun ta yanke hukuncin cewa INEC ta yi wa CDA rijista tare da ba ta takardar shaidar zama jam’iyyar siyasa cikin kwanaki bakwai.