Ƙungiyar SERAP ta buƙaci Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, da Kakakin Majalisar Wakilai, Tajudeen Abbas, da su miƙa zarge-zargen karkatar da kuɗaɗen ayyukan mazabu ko rashin bayar da bayanin yadda aka kashe sama da naira biliyan 6.3 ga hukumomin yaƙi da cin hanci da rashawa domin gudanar da bincike tare da yiwuwar gurfanar da waɗanda ake zargi.
Ƙungiyar ta kuma buƙaci shugabannin Majalisar Dokoki ta Ƙasa su tabbatar da cewa duk wanda aka samu da laifi an gurfanar da shi a kotu idan akwai isassun hujjojin da doka ta amince da su. Haka kuma ta nemi a kwato duk wasu kuɗaɗen gwamnati da aka karkatar ko aka kasa bayyana yadda aka kashe su, sannan a mayar da su cikin baitul malin gwamnati.
A cikin wata wasiƙa mai kwanan watan 27 ga Yuni, 2026, wadda Mataimakin Daraktan SERAP, Kolawole Oluwadare, ya sanya wa hannu, ƙungiyar ta ce waɗannan zarge-zargen suna kunshe ne a cikin Rahoton Shekara-shekara na Babban Mai Binciken Kuɗaɗen Tarayya na shekarar 2022, wanda aka wallafa a ranar 9 ga Satumba, 2025.
SERAP ta bayyana hakan ne cikin wata sanarwa da Oluwadare ya sanya wa hannu kuma aka fitar a ranar Lahadi.