Yayin da jam'iyyun siyasa suka kammala zaɓen fitar da gwanayensu domin tunkarar zaɓen shugaban ƙasa na 2027, wasu na ƙoƙarin hasashen sakamakon zaɓen ta hanyar duba abin da ya faru a 2023.

Sai dai masana da masu sharhin siyasa sun yi nuni da cewa ba daidai ba ne a ɗauki sakamakon zaɓen 2023 a matsayin tabbacin abin da zai faru a 2027. Sun ce sauye-sauyen siyasa, haɗakar jam'iyyu, da yanayin da ƙasa za ta kasance a lokacin zaɓe na iya sauya yadda masu kaɗa ƙuri'a za su yanke hukunci.

Ana sa ran gudanar da zaɓen shugaban ƙasa na Najeriya a watan Janairun 2027, inda ake ci gaba da bibiyar yadda yanayin siyasar ƙasar ke sauyawa.