Ɗaya daga cikin ɓangarorin da ke rikici kan shugabancin jam'iyyar ADC, ƙarƙashin Nafi'u Bala Gombe, ya ce har yanzu suna ci gaba da ƙalubalantar shugabancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark, duk da hukuncin da Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta yanke.
Da yake zantawa da BBC Hausa, Nafi'u Bala ya ce har yanzu suna da ƙara a gaban kotu da ke ƙalubalantar sahihancin shugabancin David Mark, yana mai cewa mutanen da ke jagorantar jam'iyyar a yanzu ba halastattun mambobi ba ne.
"Mu ne halastattun shugabannin jam'iyyar, kuma muna da ƙara da ke ƙalubalantar wannan shugabanci, da kuma sahihancin kasancewarsu mambobin jam'iyyar masu rajista," in ji Bala.
Jam'iyyar ADC ta shiga rikicin cikin gida ne bayan wasu manyan ƴan adawar Najeriya suka rungume ta a matsayin dandalin da za su fafata da jam'iyyar APC mai mulki a babban zaɓen 2027, lamarin da ya haifar da takaddama kan shugabancin jam'iyyar.
A ranar Alhamis, Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin David Mark, bayan ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar.
Mai shari'a Musa Liman ya yanke cewa rikicin na cikin gida ne na jam'iyyar, sannan ya ce Abejide ba shi da hurumin shigar da ƙarar saboda ya kasa nuna yadda shugabancin jam'iyyar ya take masa haƙƙinsa.
Sai dai Nafi'u Bala ya ce hukuncin da aka yanke bai shafi ƙarar da ɓangarensu ya shigar ba, yana mai jaddada cewa za su ci gaba da neman kotu ta warware rikicin shugabancin jam'iyyar.